Ma'aikatar Shari'ar Amurka Zata Binciki Rundunar 'Yansandan Chicago

Loretta Lynch sakatariar harkokin shari'ar Amurka kuma Antoni Janar din kasar

Amurka ta dade tana fama da yadda 'yansandan wasu garuruwa suke cin zarafin mutane musamman bakar fata saboda haka sabbin bayanai da suka fito daga Chicago sun tada hankalin sakatariyar harkokin shari'ar Amurka

Ministan shari'a kuma Antoni Janar ta Amurka Loretta Lynch, ta fada jiya Litinin cewa, ma'aikatar shari'a zata binciki rundunar 'Yansanda dake birnin Chicago, domin gano ko rundunar sannu a hankali tana keta tsarin mulki ta wajen amfani da karfin tsiya kan mutane.

Wannan matakin ya biyo bayan sakin wani fefen bidiyo watan jiya, wanda ya nuna yadda wani jami'in 'Yansanda ya harbe ya kashe wani matashi bakar fata dan shekaru 17 da haifuwa. Lamarin ya auku ne cikin watan Oktoban bara.