Mai Taimaka Wa Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya Kan Harkokin Yada Labarai, Isa Mohammed, Ya Rasu.

Sanata Ahmed Lawan

Kungiyar 'yan Jarada a Najeriya (NUJ), na makokin rasuwar daya daga cikin hamshakan mambobinta, Mai Taimaka Ma Shugaban Majalisar Dattawa Kan Harkokin Yada Labarai.

Mai Taimakawa Na Musamman Ma Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya Kan Harkokin Yada Labarai, Malam Mohammed Isa, ya rasu ranar Jumma’a, a cewar kafafen yada labarai, ciki da Premium Times.

Ola Awoniyi, Mai Bayar Da Shawara Na Musamman Ga Shugaban Majalisar Dattawa Kan Harkokin Yada Labarai, ya bayyana a Abuja jiya Asabar cewa, Malam Isa ya rasu ne yayin da ake masa jinyar raunukan da ya ji bayan wani hatsarin mota da ya yi a kan hanyar Mina zuwa Abuja a jihar Neja.

Mr. Awonyi ya ce tuni aka yi jana’izar mamacin a Funtua, jihar Katsina kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

A halin da ake ciki, Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Sanata Ahmed Lawan, ya yi ta’aziyya ga iyalai, da abokan aikin mamacin. Ya kuma yi ta’aziyya ma Kungiyar ‘Yan Jaridar Najeriya (NUJ) kan wannan babban rashin. Haka zalika ya yi ta’aziyya ga gwamnatin jihar Katsina da jama’ar jihar baki daya, saboda da rasuwar Malam Isa.

-PremiumTimes