Nadin Sabon Shugaban Hukumar DSS Ya Bar Baya Da Kura

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari

Shugaban kasar Najeriya ya amince da nada Yusuf Magaji Bichi a matsayin sabon darakta janar na hukumar tsaron farin kaya ta DSS . Dan asalin jihar Kano ya samu horon aiki a Birtaniya ya kuma rike daraktan hukumar ta DSS a jihohin Jigawa Neja Sokoto da Abia.

Sai dai gamayyar dattawan kudancin Najeriya da na 'yan tsakiyar kasar sunki amincewa da wannan nadi, inda suka zargi gwamnatin Buhari da fifita 'yan arewacin najeriya.

A cikin wata sanarwa da suka fitar tace daga yanzu jama'ar kudancin Najeriya sunyi wa gwamnnatin Buhari yankan kauna ganin yadda aka cire dan kudancin kasar aka maye gurbin sa da dan Arewa.

Domin Karin bayani, saurari Rahoton Hassan Maina Kaina..

Your browser doesn’t support HTML5

Jama'ar Tsakiya Da Kudancin Najeriya Basiu Amince Da Nadin Sabon Daraktan Hukumar DSS Ba- 2'47"