Nelson Mandela Ya Rasu

Tsohon shugaban Afrika ta Kudu Nelson Mandela

Shugaban Afirka Ta Kudu bakin fata na farko Nelson Mandela wanda ya yi fafaitikar yakar mulkin wariyar launi a kasar ya rasu yana da shekaru 95.
Tsohon shugaban Afirka Ta Kudu kuma bakin fata na farko wanda ya yi gwagwarmaya da mulkin wariyar launi, Nelson Mandela, ya rasu yau a gidansa dake cikin birnin Johannesburg yana da shekaru casa'in da biyar.