Jihar Ondo da ke kudu maso yammacin Najeriya ta bayyana samun mutum na farko da ya kamu da cutar coronavirus.
Gwamna Oluwarotimi Akeredolu ne ya bayyana hakan a shafinsa na Twitter a ranar Juma’a.
“A yammacin yau mun samu bayanai kan mutum na farko da ke dauke da cutar #COVID-19 a jihar Ondo. Tuni an killace shi za kuma a ba shi kulawa.” Ekeredolu ya ce.
We have just received confirmation of our first positive #COVIDー19 case in Ondo State this evening. The infected person is currently under isolation and will be monitored. We have activated all necessary protocol to locate all contacts and will be working closely with @NCDCgov.
— Arakunrin Akeredolu (@RotimiAkeredolu) April 3, 2020
Jaridar Daily Trust wacce ita ma ta ruwaito labarin ta ce mutumin da aka samu dauke da cutar soja ne da ya dawo daga India, ko da yake hukumomin jihar ba su tabbatar da hakan ba.
A halin da ake ciki gwamna Ekeredolu ya ce ana kokarin gano mutanen da mutumin ya yi mu’amulla da su domin a killace su.