Pakistan Ta Yiwa Afghanistan Tayin Tattaunawar Zaman Lafiya

FILE - Pakistani Prime Minister Nawaz Sharif will meet with King Salman on Monday in Riyadh and with Iranian President Hassan Rouhani on Tuesday in Tehran.

Kasar Pakistan ta yi kira ga Shugabannin kasar Afghanistan da su sake nazarin abin da ta kira, "matakan tattaunawar samar da zaman lafiya marasa tsari" da Taliban da ake yi don kawo karshen tashe-tashen hankulan, a maimakon dora ma Pakistan laifi dangane da tabarbarewar yanayin tsaro a Afghanistan.

Sartaj Aziz, babban mai bai wa Firaministan Pakistan Shawara kan harkokin waje, shi ne ya bayyana hakan a wata hirarsa da Muryar Amurka, inda ya kara da cewa rashin niyya a siyasance da kuma rashin tsari da Afghanistan ke fama da shi game batun Taliban - kan ko ta dau kungiyar a matsayin 'yan ta'adda ko kuma masu ruwa da tsaki a harkokin siyasar kasar na kawo cikas ga kokarin da ake yi daga ta ciki na fara tattaunwar zaman lafiya tsakanin bangarorin da ke yaki da juna a Afghanistan.