Shugaba Buhari Zai Tsabtace Yankin Niger Delta.

Shugaba Buhari da takwaran aikins a na Afirka ta kudu Jacob Zuma.

Ministan kasa Alhaji Ibrahim Usman Jibril ne ya bayyana haka lokacinda ya kawo ziyara Muriyar Amurka.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, yana shirin fara gagarumin aikin tsabtace muhalli a yankin Niger Delta mai arzikin mai, yankin da ya juma yan fama da matsalar gurbatar muhalli.

Ministan kasa a ma'aikatar kare muhalli Alhaji Ibrahim Usman Jibril ne, ya bayyana haka a lokacinda ya kawo ziyara anan Muriyar Amurka.

Ministan yace shugaba Buhari ya dukufa wajen warware kalubale da kasar take fuskanta ta fuskar muhalli.

Ministan yace saboda haka ne ma shugaban ya dora musu nauyin maida hanklai kan batun muhalli da zummar samar da ayyukan yi,kare muhalli da kuma ci gaban kasa.