‘’Wannan barikin yana da muhimmaci kwarai da gaske idan aka kwatantashi da matsalolin da ake samu game da yin wannan yakin da sojan sama suke yi a gabashin arewa maso gabas na Najeriya wannan sansani da za ‘a bude a Bauci zai taimaka kwarai da gaske maimakon inda ake tashi yanzu za a iya tashi daga Bauci kuma zaiyi sauki a iya gudanar da ayyukan nan da muka sa gaba Insha ALLAHU, mun riga munyi nada kwamanda anan da sauran manyan jamiian sojoji da zasu shigo Bauci kuma mai girma gwamnan jihasrBauci ya bamu gudunmowar gidaje harm un gyara su saboda ofisoshi da sauran sojojin sunzo sun fara aiki tun ma kafin a kare gini’’
Yaci gaba da cewa suna fatan lokacin da suka kare aikin gina wannan tashan sauka da tashin jiragen wau jiragen su za a dawo dasu nan kana zasu samu asibiti wanda asibitin zai taimaka ma harda mutanen kauyukan dake kewaye da tashan jirgi .
Ga Abdulwahab Mohammed da Karin bayani
Your browser doesn’t support HTML5