Sojojin Nijar Da Faransa Sun Yi Nasarar Kashe 'Yan Ta'adda 120

Sojojin Kasar Nijar

Sojojin Kasar Nijar

Ma’aikatar tsaron Jamhuriyar Nijar ta sanar da cewa dakarun tsaron kasar sun samu nasarori sosai, a rawar dajin da suka kaddamar a farkon watan nan na Fabarairu, da hadin gwiwar sojojin rundunar Barkhane a Arewacin yankin Tilabery, a iyakar Mali da Nijar, inda suka hallaka ‘yan ta’adda sama da 100 tare da kama tarin makamai da babura.

Sojojin Kasar Nijar

Sojojin Kasar Nijar

Tun a ranar 1 ga watan Fabarairu ne sojojin Nijar da takwarorinsu na Faransa, suka kai wani farmaki a Arewacin yankin Tilabery, da kan iyakar Mali da Nijar abinda ya basu damar hallaka ‘yan ta’adda kimanin 120.

'Yan ta'adda 23 daga cikinsu, sun fada tarko sojojin hadin gwiwar ne a kauyukan Inates, Tongo-Tongo, da Tiloa inji sanarwar ma’aikatar tsaro. Wacce ta kara da cewa dakarun sun kama babura 10, hade da wasu kayayyakin hada boma-bomai. Wani dan jam’iyya mai mulki Assoumana Mahamadou, ya bayyana farin cikinsa da jin wannan labarin.

A ra'ayin wani dan adawa Ibrahima Diakite, canjin shugabancin da aka samar a rundunar mayakan kasar Nijar a tsakiyar watan jiya ne ya fara bayar da irin wannan kyakkyawan sakamakon.

Kasar Faransa wacce ta girke dubban sojoji da sunan yaki da ta’addanci a yankin Sahel, ta sha suka daga jami’an fafutika a kasashen Mali, Nijar, da Burkina Faso a watannin baya.

Saboda zargin cewa ba sa tabuka wani abin a zo a gani. Abinda ya sa jami’in fafutika Salissou Amadou ya ce wannan gwagwarmayar ce ta fara tasiri a wajen hukumomin Faransa.

A yanzu dai ‘yan kasa sun zuba ido don ganin irin abubuwan da bincike a ma’aikatar tsaron Nijar ya gano, game da dalilan da ake zargin sune suka hana ruwa gudu a yakin, da Nijer ta kaddamar kan kungiyoyin ta'addancin Mali.

A saurari rahoto cikin sauti daga birnin Yamai a Jamhuriyar Nijar.

Your browser doesn’t support HTML5

Sojojin Nijar Da Faransa Sun Yi Nasarar Kashe 'Yan Ta'adda 120