Super Falcons Ta Cancanci Yabo – Remi Tinubu

'Yan wasan Super Falcons suna murnar zura kwallo (Hoto: Facebook/Super Falcons)

Rabon da tawagar mata ta Najeriya ta je gasar tun shekaru 16 da suka gabata.

Uwargidan Shugaban Najeriya, Remi Tinubu ta yabi ‘yan wasan Super Falcons bayan da suka samu gurbin zuwa gasar wasannin Olympics da za a yi a Paris.

Rabon da tawagar mata ta Najeriya ta je gasar tun shekaru 16 da suka gabata.

“Kawo karshen rashin zuwa gasar wasannin Olympics da aka kwashe shekaru 16 ba a je ba, ba karamar nasara ba ce.

“Jajircewarku da nuna juriya da yin aiki tare sun sa Najeriya tana mai alfahari tare da kwadaitar da ‘yan mata da babu adadi a sassan kasar nan.” Remi Tinubu ta ce a cikin wata sanarwa da ta fitar a kafafen sada zumunta.

A ranar Talata tawagar ‘yan wasan ta mata karkashin jagoranci mai horarwa Randy Waldrum ta yi nasara akan ‘yan wasan Afirka ta Kudu Bayana-Bayan bayan da aka yi jimullar kwalaye da ci 1-0 a wasanni biyu da suka buga.

A wasan da aka buga a Abuja a makon da ya gabata, Super Falcons ta yi nasara da ci 1-0 yayin da aka tashi canjaras a wasan da suka buga a Pretoria a ranar Talata.

Najeriya tana rukunin 'C' mai dauke da Sifaniya, Japan da Brazil.

Lokaci na karshe da Super Falcons ta je gasar tun wanda aka yi a shekarar 2008 a Beijing.

C