Tanzania: An Mayar Da 'Yan Gudun Hijirar Burundi 500 Gida

FILE - Refugees who fled Burundi's violence and political tensions wait to board a U.N. ship, at Kagunga on Lake Tanganyika, Tanzania, to be taken to the port city of Kigoma, May 23, 2015.

Fiye da 'yan kasar Burundi 500 ne aka maida da su kasarsu daga sansanonin 'yan gudun hijira guda uku da ke Tanzaniya a jiya Alhamis, matakin da ya zama na farko a gagarumin yunkurin da ake yi don mayar da mutanen da ke tserewa tashin hankali da rikice-rikice a shekarun baya zuwa kasashensu.

An saka kasar 'Yan Burundi a motocin bas-bas a sansanin Nduta, Mutendeli da Nyarugusu da ke yammacin Tanzania, inda za a dangana da su har zuwa wasu cibiyoyin karbar baki biyu a Lardin Ruyigi da ke kasarsu.

Bayan kuma sun kwana, za a tura su zuwa gidajensu a Lardunansu.

Hukumar Kula da 'Yan Gudun Hijira ta Majalisar Dinkin Duniya ta yi kiyasin cewa, sansanonin na Tanzaniya suna dauke da 'yan kasar Burundi kusan 184,000 wadanda za a tura su gida nan da karshen shekara nan, bisa yarjejeniyar da kasashen biyu suka kulla.

Suna kuma daga cikin ‘yan kasar Burundi kusan 350,000 da suka tsere wa rikicin siyasa a Gabas ta Tsakiya, wanda ya barke bayan wani zaben mai cike da takaddama da aka yi a shekarar 2015.