Jiya Lahadi da yamma ne Sanata Isiyaka Adeleke ya fara nuna zazzabi a garinsa Ede nan take kuma a garzaya dashi asibiti a garin Oshogbo babban birnin jihar inda rai yayi halinsa
WASHINGTON DC —
An haifi Sanata Isiyaka Adeleke a Enugu ranar 15 ga watan Janairu na shekarar 1955.
Shi dai Sanata Adeleke ya karanta digiri na farko da na biyu a fannin mulkin jama'a.
A lokacin rayuwarsa marigayin ya rike mukamai da dama.
Mazauna jihar Osun sun nuna juyayi bisa ga rasuwar Sanata Isiyaka Adeleke. Suna mai cewa sun yi rashi babba. Sun ce mutum ne nagari saboda yayi abubuwan cigaba.
Ga rahoton Hassan Umaru Tambuwal da karin bayani.
Your browser doesn’t support HTML5