Wani Dan Shekara 8 da Ya Gudu Daga Maiduguri Da Iyayensa

Wani yaro dan aji 2 firamare ya bayyana dalilansu na gudu daga Maiduguri, da abubuwan da suka gani kan hanyarsu ta zuwa Gombe
Wannan dan yaro mai shekara 8 da haihuwa ya bayyanawa wakilin Sashen Hausa na Muryar Amurka, Abdulwahab Muhammad, irin abubuwan da suka gani a kan hanyarsu ta zuwa Gombe tare da iyayensa, a bayan da suka gudo daga Maiduguri.

Wannan ya biyo bayan dokar ta bacin da aka kafa a can, da kuma sabbin matakan tsaron da ake dauka wadanda suka jefa jama'a cikin yanayi na lahaula.

Your browser doesn’t support HTML5

Wani Yaro mai Shekara 8 Da Haihuwa da Yayi Hijira Tare Da Iyayensa Daga Maiduguri Zuwa Gombe