'Yan Super Eagles Za Su Yi Galaba Akan Iran Inji Darektan Wasannin Jahar Bauchi Haruna Bako

Magoya bayan 'yan wasan kwallon kafar Najeriya na Super Eagles na yi mus u kaimi a fagen wasa

Haruna Bako ya ce Najeriya za ta yiwa Iran ci 2-1 ko kuma ci 2-0
Yau da misalin karfe uku na rana ne agogon mu na nan Washington D.C, wato 9 kenan na dare agogon Najeriya, kungiyar 'yan wasan kwallon kafar Najeriya ta Super Eagles ta ke fara wasan ta na farko a gasar cin kofin duniya, inda zata fafata da kasar. Saboda haka Bello Habeeb Galadanchi ya tuntubi Alhaji Haruna Bako, darektan wasanni na Jahar Bauchi, domin jin ko me ake tsammanin gani a wannan wasa?

Your browser doesn’t support HTML5

Bayanin Haruna Bako kan wasan Najeriya a kasar Brazil.-3':23"