'Yan Wasan Najeriya Zasu Kai Labari Kuwa?

Ahmed Musa dan wasan Najeriya.

Najeriya,yau zata buga wasan ta na farko da kasar Iran,a gasar cin kofin kwallon kafa na duniya, da ake gudanarwa a Brazil, da karfe 8.00pm na dare agogon Najeriya .

Najeriya da Iran nayiwa juna kallon-kallo, koda yake doke Iran zai taimakawa Najeriya domin ta samu ta ci gaba a rugunin da take.

Ghana, kuwa zata buga nata da kasar Amurka, da karfe 11.00pm na dare agogon Najeriya.

Inda za’a iya tunawa so biyu ‘yan wasan kwallon kafa ta kasar Ghana, suke jawa ‘yan wasan kwallon kafa na Amurka biriki na hanasu kaiwa sagaye na gaba a tarihin kasar cin kofin kwallon kafa ta duniya.

A gasar cin kofin kwallon kafa na duniya da aka buga a kasar Jamus, a shekaran 2006 Ghana,ta doke Amurka da ci 2 da 1,wanda aka buga ma a kasar Afirka ta kudu shekaru hudu da suka wuce shima Ghana ta doke Amurka da ci 2 da 1.

Najeriya zata yi rawar gani kuwa? - 1'00"