Za a Rantsar Da Sabon Shugaba a Burundi Ranar Alhamis

Evariste Ndayishimiye

Ranar Alhamis ne ake sa ran za’a rantsar da shugaban kasar Burundi da aka zaba, Evariste Ndayishimiye, mako daya bayan rasuwar shugaban kasar mai barin gado Pierre Nkurunziza, a cewar kafafen yada labaran kasar.

A makon jiya ne kotun tsarin Mulki ta yanke hukuncin cewa a rantsar da shugaban da aka zaba ba tare da bata lokaci ba.

Jam’iyar CNDD-FDD ce ta zabi Ndayashimiye da ya gaji Nkurunziza.

Ya yi nasarar samun kuri’u kashi 60 cikin dari a zaben na watan Mayu, wanda jam’iyar adawa da bata yi nasara ba ta yi zargin cewa, ya na cike da magudi.

Ndayashimiye zaiyi wa’adin shekara 7 ne kafin ya tsayawa takara a sake zabar sa.