An kama Seyni Amadou, babban editan gidan talabijin na Canal 4, in ji kungiyar CAP-Medias-Niger, mai wakiltar ma'aikatan yada labarai a kasar. A ranar Juma'ar da ta gabata ma'aikatar sadarwa ta Nijar ta sanar da dakatar da tashar ta shi na tsawon wata guda.
Trump ya shaida wa gidan talabijin na NBC a wata hira cewa, "wasu karin kwanaki 90 wani abu ne da za’a iya yi, domin abu ne da ya dace."
A yau Lahadi an tsara Trump zai halarci bikin shimfida furanni a makabartar Arlington, kafin ya nufi wani gangami a dandalin Capital One Arena da ke Washington.
Ya zuwa safiyar Assabar, an sami shawo kan kashi 43% na harsunan wutar Palisades, wanda ya karu daga kashi 31% na ci gaban da aka samu a ranar Juma'a, a cewar Ma'aikatar Gandun daji da Kariyar gobara ta jihar California.
Murabus din na Smith wata alama ce ta rugujewar tuhume-tuhumen da ake yi wa Trump, wadanda ke iya ƙarewa ba tare da wani sakamako na shari'a ba ga shugaban kasar mai jiran gado.
Jami'ai sun yi gargadin cewa adadin wadanda suka mutu, wanda aka sabunta shi a yammacin ranar Alhamis, na iya karuwa, idan aka sami shawo kan gobarar mai dimbin harsuna daban-daban, inda ma'aikata za su iya karade wurin da ta mamaye.
An zargi dakarun tsaron kasar wadda ke yankin gabashin Afirka da kamawa da tsare mutane da dama ba bisa ka'ida ba, tun bayan zanga-zangar adawa da gwamnati da matasa suka yi a watannin Yuni da Yuli.
Darakta-Janar na hukumar ta WHO Tedros Adhanom Ghebreyesus, ya ce bama-baman da suka fada kan ginin suna da matukar ta da hankali, ta yadda kunnuwansa suka yi ta rugugi har ‘yan kwanaki bayan harin.
Matambaya daga cikin tsoffin ‘yan tada kayar bayan da suka sami kwace iko da Damascus a ranar 8 ga watan Disamba, sun gana da tsoffin sojojin tare da ba su jerin tambayoyi da lambar rajista. An kuma ba su damar su tafi abinsu.
A yayin wani taron manema labarai, Macron ya yi marhabin da yarjejeniyar Ankara da Jamhuriyar Dimokaradiyyar Habasha da kuma Tarayyar Somaliya suka cimma a ranar 11 ga watan Disamba.
An kada kuri’un amincewa 366 da suka rinjayi na kin amincewa 34, inda dan majalisa guda kuma bai da kowane ra’ayi. Dukkanin kuri'u 34 da suka nuna adawa da kudirin na 'yan jam’iyyar Republican ne.
Jami'an Ukraine sun ce harin ya biyo ne bayan harin makami mai linzami da Rasha ta fara kai wa a Kyiv.
Karar wadda aka shigar a ranar 19 ga watan Maris a Kotun Gunduma ta Amurka da ke Kudancin Florida, ta zargi Stephanopoulos ABC News da yin munanan kalamai kan Trump tare da mummunar manufa da kaucewa gaskiya.
Zafafar wannan fadan na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban kasar Congo Felix Tshisekedi, da na Rwanda Paul Kagame za su gana a yau Lahadi a kasar Angola, wadda ke shiga tsakani a rikicin.
Domin Kari