Mambobin Kungiyar Kwadago ta Najeriya wato NLC sun gudanar da zanga-zanga a fadin kasar sakamakon matsin rayuwa, yunwa da tabarbarewar tattalin arziki a kasar.
Wasu yanbindiga sun hallaka mutane 3 tare da yin garkuwa da kimanin mutanen 30 a jihar Neja dake Arewa maso tsakiyar Najeriya.
Masu kamfanonin buredi a Najeriya sun ce suna daf da rufe kamfanoninsu saboda matsalar tashin gwauron zabi da kayan sarrafa buredin ke yi a halin yanzu.
Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce ta kama wasu mata guda uku da ake zargin suna da hannu wajen shirya zanga-zangar tsadar rayuwa da aka gudanar a jihar Neja a ranar Litanin din nan da ta gabata.
A yayin da ‘yan Najeriya ke ci gaba da kokawa kan tsananin tsadar rayuwa a kasar, suma ‘yan jaridun kasar sun ce suna cikin yanayi na tsaka mai wuya musamman yadda aikinsu na kokarin ankarar da gwamnati halin da ‘yan kasar ke ciki da kuma hanyoyin shawo kan matsalolin da suke fuskanta.
Shugaban Hukumar Kwallon Kafa ta Nigeria Alh. Ibrahim Gusau yace bashi da wani shakku akan wasan da Super Eagle zata kara da mai masaukin baki a gasar cin kofin Afrika da a ke yi yanzu haka a kasar Kwaddebuwa.
A wani rahoton da Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta jihar Neja ta fitar a karshen shekara ta 2023 ya nuna cewa da ga shekarar 2017 zuwa wannan lokaci sama da garuruwa 335 ne Mutanensu suka tarwatse a cikin kananan Hukumomi 14 na jihar Nejan saboda Matsalar Hare Haren yanfashin Dajin
‘Yan kabilar Kambari a Nigeria sun gudanar da babban taronsu na karshen shekara, tare da janyo hankalin ‘yan kabilar kan muhimmancin zaman lafiya da kuma kaunar juna.
“Shawarana shine gwamnati ta manta da manya manyan ayuka. Ta mayar da hankali wurin tsaro. Saboda in ka kaddamar da babban aiki amma babu tsaro, ba abunda ka yi. Tafiyar ma ya zama wahala”, a cewarsa.
Iyalan marigayi Alhaji Kabiru Muhammad daga jihar Naija sun ce har yanzu ba su ji komai ba dangane da batun biyan diyyar marigayin, wanda ya rasu a kasar Saudiyya, sanadiyyar makalewa a cikin na'urar da ke kai mutane gidan sama da ta lalace.
Gwamnan jihar Umar Muhammad Bago, ya bayar da wannan umurni ne a wani jawabi da ya gabatar a lokacin kaddamar da wani aikin noman shinkafa a jihar a ranar Lahadi.
Al’ummomin kasashen Jamhoriyar Nijar da Najeriya na ci gaba da yin kiraye kirayen ganin an bude bodar kasar Nijar tare da janye takunkumin da aka kakaba wa kasar ta Nijar bayan juyin mulkin da sojoji su ka yi a ranar 26 ga watan Yuli.
Rundunar sojojin Najeriya ta kammala wani atisayen makwanni biyu da ta yi wa lakabi da “Operation Mugun Bugu” wanda shine na biyu a wannan shekara ta 2023.
Hukumar zaben Najeriya ta ayyana Alhaji Ahmed Usman Ododo na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar Kogi da aka gudanar ranar Asabar.
Daruruwan ‘yan jihar Kogin Najeriya ne suka nufi rumfunan zabe domin kada kuri’arsu ta zaben sabon gwamnan jihar a ranar Asabar, da zai yi mulki jihar na tsawon shekaru hudu nan gaba.
Zaben na jihar Kogi za a gudanar da shi ne tare da na jihohin Imo da Bayelsa da ke kudancin kasar.
Gwamnatin jihar Nejan Najeriya ta ce ta na shirin tafiya kotu idan har gwamnatin Najeriya ta ki ba ta kaso 13 na kudaden da ake samu daga tashoshin samar da hasken lantarki dake jihar.
Yanzu haka dai matsalar rashin tsaro na ci gaba da jefa daruruwan mazauna yankunan karkara cikin tashin hankali a sassa dabam daban na jihar Neja a Najeriya.
Kungiyar Zabarmawa mazauna Najeriya ta nuna rashin amincewa da kai harin soja a Nijar bayan juyin mulki da sojoji suka yi a watan Yuli.
Domin Kari