Gwamnatin jihar Kogi tace tana gudanar da bincike akan wasu manyan sarakunan jihar guda 2, game da wani mummunan tashin hankalin da yayi sanadiyyar mutuwar kimanin mutane 9 tare da kona gidaje da dama a 'yan kwanakin da suka gabata a karamar hukumar Bassa dake cikin jihar Kogin.
Gwamnatin jihar Kwaran dai ta ce tana damawa da kowa a jihar sai dai watakila Hausawan ne ke yin baya-baya a shiga harkokin siyasar jihar.
Mahara dauke da manyan bindigogi akan babura sun auka a garin Gidigori a karamar Hukumar Rafi inda Bayan sun hallaka mutane sun kuma kona gidaje tare da yin garkuwa da wasu mutanen garin da dama,
A yanzu haka dai daruruwan mutane ne suka tsere daga garuruwansu a sakamakon wani sabon harin ‘yan bindiga a jihar Neja da ke arewa ta Tsakiyar Najeriya.
Babbar jam’iyyar adawa ta PDP ta kasa gudanar da zabenta na fidda gwani na masu takarar kujerar gwamna da ta shirya gudanarwa a ranar laraban nan a jihar Neja. Al’amarin da ya raba kan 'yaƴan jam’iyyar ta PDP gida 2.
'Ƴan siyasa da Masana Harkokin shari’a na ci gaba da yin sharhi dangane da jinkirin sanya hannu akan kwaskwarimar dokar zaben Nigeria da Shugaban kasar Muhammadu Buhari ke yi.
Hukumomi da shugabannin Addinai sun dukufa wajan fadakarwa akan kai zuciya nesa a garin Tungan Magajiya ta Karamar Rijau a jihar Nejan Nigeria.
Ayayin da Hada hadar Siyasa ke ci gaba da kan kama a Nigeria masu ruwa da tsaki akan harkokin siyasar na ci gaba da nuna bukatar ganin jam'iyyun siyasar sun yi adalci a lokacin zaɓuɓbukan tsaida yantakara na jam'iyyun siyasa,
Shugabanni a jihar Nejan Najeriya sun yi amfani da bukukuwan karamar sallah wajen tunatarwa akan muhimmancin zaman lafiya da neman sauki akan matsalar 'yan bindiga da suka addabi jihar.
Babbar jam,iyyar Adawa ta PDP a Najeriya ta hana wasu ‘yan takara mukamin majalisun dokokin kasar su guda biyar da suke neman tsayawa takara a jam’iyyar daga jihar Neja.
A yanzu haka dai kamfanin samar da hasken lantarki na Abuja wato AEDC ya katse wutar lantarki a wasu ofisoshin gwamnatin jihar a ciki harda ofishin sakataren gwamnatin jihar,
A ci gaba da tabbatar da kwanciyar hankali da shugabannin al'umma ke yi albarkacin lokacin da ake ciki na yawaita ayyukan alkhairi, wasu magabata na wata hobbasa ta sake hade bangarorin kungiyar Izala ta Najeriya wuri guda.
'Yan siyasa a Najeriya na ci gaba da bayyana matsayinsu na shiga takarar neman mukamai daban-daban a babban zaben kasar dake tafe a shekara ta 2023.
An shafe kimanin shekaru 4 da zamansa garin Phata-Kacha dake yankin karamar hukumar Mokwa ta jihar Neja kango, tun bayan da wani rikicin neman mallakar fili tsakaninsu da mutanen garin Kacha yayi sanadiyyar tarwatsa kauyen.
A jihar Nejan Najeriya dubban 'yan gudun Hijira ne da 'yan bindiga suka raba da muhallansu ke cikin wani mawuyacin hali a wannan wata na Ramadana.
Masu aikin ceto na can na neman wasu mutane da ba a tantance yawan su ba da wani jirgin ruwan kwale kwale ya kife dasu a jihar Neja.
Hukumomi a jihar Kogin Najeriya na gudanar da bincike akan wasu matasa da ake zargin ‘yan kungiyar matsafane da suka addabi birnin Lokoja fadar gwamnatin Jihar.
Shirin dai a karkashin hukumar nan ta kula da tasoshin samar da wutar lantarki a Najeriya wato HYPADEC zai horar da matasan da suka kammala karatunsu na boko amma kuma ba su da aikin yi da hakan zai taimaka wajen rage aikata miyagun ayyuka a kasa.
Gamayyar Jami’an tsaron Nigeria sun samu nasarar tarwatsa wasu ‘yan bindiga da suka kai hari a wani ofishin ‘yan sanda na jihar Nejan Najeriya.
Wasu 'yan bindiga sun hallaka wani babban jami’in ‘yan sanda wato DPO tare da wasu jami’an tsaro guda takwas a jihar Neja dake Arewacin Najeriya.
Domin Kari