Jami’an sunce wadanan kalaman na “bacin rai ne” kuma masu iya bata dangatakar dake tsakanin kasashen da abin ya shafa.
A shekaran jiya Laraba ne Mr. Erdogan yake gayawa wani dandandalin Majalisar Dinkin Duniya da aka kira a birnin Vienna cewa “in dai har za’a dauki Musulunci laifi ne”, to ita ma akidar yahudanci ya kamata yi mata daukar laifi.