WASHINGTON, D.C - Ana tuhumar Ntaganda da laifukkan yaki guda bakwai da kuma laifukka ukku na gallazawa Bil Adama.
Lauyoyin kotun ta ICC sun ce a matsayinsa na kwamandan mayakan ‘yantawayen Junhuriyar Demokradiyar Congo, shine yake da alhakin cusa yara kanana cikin yakin bada son ransu ba da kashe-kashen gilla da fyaden da aka yi wa mata da yawa.
Manufar wannan zaman Kotun na yau dai shine don a bayyanawa Ntaganda laifukkan da ake tuhumarsa da aikatawa da kuma a tsaida ranar da za’a soma ainihin ita shara’ar tashi.
A cikin makon jiya ne dai Ntaganda ya kai kansa opishin jakadancin Amurka dake Rwanda, ya nemi a aika shi zuwa kotun ta ICC dake Hague.
Lauyoyin kotun ta ICC sun ce a matsayinsa na kwamandan mayakan ‘yantawayen Junhuriyar Demokradiyar Congo, shine yake da alhakin cusa yara kanana cikin yakin bada son ransu ba da kashe-kashen gilla da fyaden da aka yi wa mata da yawa.
Manufar wannan zaman Kotun na yau dai shine don a bayyanawa Ntaganda laifukkan da ake tuhumarsa da aikatawa da kuma a tsaida ranar da za’a soma ainihin ita shara’ar tashi.
A cikin makon jiya ne dai Ntaganda ya kai kansa opishin jakadancin Amurka dake Rwanda, ya nemi a aika shi zuwa kotun ta ICC dake Hague.