Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wani Dan Taliban Ya Kutsa Da Mota Cikin Tawagar 'Yan Sanda


Shedun gani da ido sun ce sun ga ‘yan sanda na kwashe gawarwakin wadanda suka mutu da wadanda suka samu raunuka

Wani dan kunar bakin waken kungiyar ta’addancin Taliban ya kutsa da wata babbar motar kunar bakin cikin wata tawagar ‘yan sanda a Kabul babban birnin kasar Afghanistan.

Inda jami’an tsaro akalla 30 suka mutu aka raunata da dama daga cikinsu. Jami’an gwamnatin Afghanistan sun ce an sami tashin bama-baman ne daya bayan daya.

Sannan shedun gani da ido sun fadawa muryar Amurka cewa sun ga ‘yan sanda na kwashe gawarwakin wadanda suka mutu da kuma dimbin wadanda suka ji rauni sakamakon tashin bama-baman.

Shugaba Ashraf Ghani yayi Allah wadai da harin, da cewa wannan wani hari ne na cin zarafin bil’adama. Ya kuma umarci ma’aikatar harkokin cikin gidan kasar da ta gudanar da binciken yadda aka shirya tafiyar jerin gwanon motocin ‘yan sandan.

Tare da alkawarin daukar matakin ladabtarwa matukar aka sami sakaci a lamarin harin da ya hallaka tare da jikkata jami’an tsaron da ke kan hanyar zuwa Kabul daga tsakiyar gabashin lardin Wardak a shirye-shiryen karamar sallah. Tuni ‘yan Taliban din suka dauki alhakin kai harin.

TASKAR VOA: Yadda Tsofaffi Ke Fama Da Lalular Yanar Ido A Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:26 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
TASKAR VOA: Fim Da Aka Shirya Kan Leah Sharibu Ya Samu Lambar Yabo
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:26 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

TASKAR VOA: Kalubalen Da Masu Fama Da Lalurar Galhanga Ke Fuskanta
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:26 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
TASKAR VOA: Tasirin Cibiyar Kula Da Lafiyar Mata Da Yara Ta HopeXchange A Ghana
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:41 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG