A kasar Sudan, a jiya talata jami’iyyun siyasa da wasu kungiyiyo 22 suka ce za su yi kira ga shugaba Omar Al-Bashir da ya yi marabus daga mukaminsa ya kuma mika iko ga wata “majalisa mai cin gashin kanta” da gwamnatin wucin gadi da za su shirya zabe karkashin turbar Dimokradiyya.