Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

DOMIN IYALI: Matan Najeriya Da Zaben 2023-Kashi Na Biyu, Yuli, 07, 2022


Alheri Grace Abdu
Alheri Grace Abdu

Idan kuna biye da mu, makon jiya muka fara nazari kan kalubalen da ke gaban mata a cimma burinsu na samun kaso 35 cikin dari na guraban siyasa a Najeriya a daidai lokacin da gangar siyasa take amo a kasar na shirin babban zabe farkon shekara badi.

Yau ma, muna tare da bakin da muka gayyata domin nazarin lamarin da neman mafita Madam Eneh Ede ‘yar fafatukar kare hakkokin mata, kuma wadda ta tsaya takara a matsayin mataimakiyar gwamna a jihar Binuwe a zaben da jam’iyarta ta sha kaye, da ‘yar gwaggwarmaya Barrister Hassana Ayuba Mairiga,, da kuma dan siyasa a jihar Kano Nasir Shuaibu Marmara.

Jagorar tattaunawar Medina Dauda, ta tambayi Barrista Hassana ko da gaske ne bayanin da Nasir Shu’aibu ya yi cewa, mata suna riga-malam Masallaci a neman mukaman siyasa ba tare da tsayawa su kware ba.

Saurari shirin domin jin amsar wannan tambaya da kuma wadansu bayanai.

DOMIN IYALI: Matan Najeriya Da Zaben 2023-Kashi Na Biyu-10:00"
please wait

No media source currently available

0:00 0:10:15 0:00

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG