Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Jam'iyyar Dake Mulkin Ivory Coast Ta Ce Zata Tsame Hannu A Shirin Samar Da Zaman Lafiya Na Majalisar Dinkin Duniya


Jam'iyyar dake mulkin kasar Ivory Coast ta ce zata tsame hannunta daga shirin wanzar da zaman lafiya da Majalisar Dinkin Duniya ke tallafawa a kasar, ta kuma yi kiran da a janye sojojin kiyaye zaman lafiya na kasashen waje daga Ivory Coast.

Jam'iyyar "Ivorian Popular Front" ta bukaci da a janye sojoji dubu bakwai na Majalisar Dinkin Duniya, da wasu dubu hudu na Faransa wadanda ke kokarin tabbatar da zaman lafiya a wannan kasa dake Afirka ta Yamma.

Jiya talata, magoya bayan shugaba Laurent Gbagbo sun yi caa a hedkwatar ayyukan kiyaye zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya dake Abidjan, suka kuma mamaye wani sansani na majalisar a birnin Guiglo.

Babban sakataren majalisar, Kofi Annan, ya bukaci da a kawo karshen abinda ya kira "tashin hankalin da ake kitsawa" kan cibiyoyin Majalisar Dinkin Duniya.

An fara zanga-zanga ranar litinin a bayan da masu shiga tsakani na kasashen waje dake samun goyon bayan majalisar suka ce ya kamata a rushe majalisar dokokin Ivory Coast saboda wa'adin aikinta ya cika a watan da ya shige.

XS
SM
MD
LG