Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Colin Powell Ya Ce Nan Bada Jimawa Ba Shugaba Bush Zai Bayyana Shirin Samar Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya - 2002-06-12


Sakataren harkokin wajen Amurka, Colin Powell, ya ce nan bada jimawa ba shugaba Bush zai bada sanarwar matakan samar da zaman lafiya a yankin Gabas ta Tsakiya, ciki har da ra'ayoyinsa kan bunkasa tsaron kasar Isra'ila tare da kafa kasar Falasdinu.

Mr. Powell bai bayyana lokacin da za a bada wannan sanarwa ba.

Amma kuma ya ce nan bada jimawa ba wannan sanarwa zata fito, a bayan shugaba Bush ya tattauna cikin wannan mako da ministan harkokin wajen kasar Sa'udiyya, Yarima Sa'ud al-Faisal.

Wannan ziyara ta ministan harkokin wajen Sa'udiyya, ita ce zata kammala tuntubar musanyar ra'ayoyin fiye da watanni biyu da Amurka tayi da shugabannin yankin Gabas ta Tsakiya.

A cikin 'yan kwanakin da suka shige, Mr. Bush ya gana da firayim minista Ariel Sharon na Isra'ila, da shugaba Hosni Mubarak na Misra.

XS
SM
MD
LG