Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

'Yan Gani Kashenin Islama A Mali, Sun Kai KUnar Bakin Wake Irinsa Na Farko


Sojojin Mali suke nazarin wata nakiya da aka gano.
Sojojin Mali suke nazarin wata nakiya da aka gano.
Sojojin Mali sun ce wani dan kunar bakin wake ya tarwatsa kansa kusa da gungun wasu sojoji, wannan shine karo na farko da yan tawayen suka fara amfani da wannan salon kai harin, tun lokacin da Faransa ta daukin matakin soji na kai farmaki kan ‘yan tawayen, cikin watan jiya.

Jami’an sun ce wani soja ya sami rauni lokacin da dan kunar bakin waken ya tunkaro wurin akan babur ya kuma tada nakiyoyin, a wani wurin da sojojin suke bincike motoci kusa da birni Gao yau jumma’a.

Dakarun faransa masu marawa dakarun Mali baya, suna fuskantar karin turjiya daga yan tawayen islamar a arewacin Mali a yan kwanakin nan, bayan da dakarun suka kwato iko a yankin a watan da ya gabata.
Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG