Karkashin tsarin ba da rancen, kowane manomi zai sami Naira 250,000 don noma kadada daya.
Daga cikin wannan kason na rancen, shirin ya tanadarwa kowannensu taki, maganin feshi, injinan ban ruwa da ingantaccen iri don kaucewa karkata kudaden zuwa biyan wasu bukatu na kansu.
Da yake kaddamar da shirin mataimakin gwamnan jihar Adamawa, Injiniya Martin Nasir Babale ya bayyana aniyar gwamnati na fadada shirin yadda kananan manoma 40,000 za su amfana ta hanyar juya kudaden bayan sun biya rancen.
Daga cikin matakan da shirin ya tanada, domin ganin manomi ya samu riba ko da farashin shinkafan ya fadi a kasuwanni akwai tsarin saye amfanin gonan kai tsaye daga hannun manoman, in ji injiniya Abubakar Aji shugaban hukumar koyar da sabbin dabarun noma ta jihar Adamawa.
Sai dai wasu daga cikin kananan manoman da sashen Hausa ya tuntuba don jin ra’ayinsu kamar irinsu Alhaji Tafida Maikano, a ganinsu an makara wajen kaddamar da shirin ana gab da sauran ‘yan makonni a shiga damina.
Ga rahoton Sanusi Adamu da karin bayani.
Facebook Forum