Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Addu'a Ga Shugaba Buhari Ita Ta Fi Mahimmanci


Majalisar yaran Najeriya, sun gudanar da addu’oi, na masamman domin neman Allah ya baiwa shugaban najeriya, Muhammadu Buhari, sauki sama da wata guda Kenan dai shugaban yake kasar Ingila inda ake duba lafiyarsa.

Mr. Patrick Ikemi, shugaban majalisar yaran Najeriya da akasarinsu ‘yan kasa da shekaru goma sha hudu ne zuwa kasa, yace yakamata ace duk kasar ne aka dukufa yin addu’a wa shugaban Najeriya, amma hakkan bai samu ba shi yasa yara suka ce ba zasu bi wannnan hanyar ba shi yasa aka tarasu a garin Minna domin gudanar da addu’oin.

Abdulrazak Idris, na daya daga cikin wadanda suka addu’oi ga shugaba Muhammadu Buhari, baya kammala sallar juma’a, a babban Masallacin juma’a na garin Minna.

Shugaban Majalisar Limaman jihar Nijar Sheikh Isa Fari, yace gudanar da addu’oin shine yafi mahimmanci a daidai wannan lokaci.

A ranar lahadi majalisar yaran sunce zasu gudanar da irin wadannan addu’oi a Coci domin neman lafiya ga shugaba Buhari.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:39 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG