Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Akalla Mutane 7 Sun Mutu A Hadarin Jirgin Ruwan Hungary


A yau juma’a masu ceto a birnin Budapest na kasar Hungary na cigaba da aikin tsamo wani jirgin ruwan yawon shakatawa daga kasan kogin Danube, yayin da suke neman mutane 21 da har yanzu ba’a gansu ba, bayan jirgin ruwan ya yi karo da wani makeken jirgin ruwa na wasu 'yan yawon shakatawa a shekaranjiya Laraba.

Sai dai ya zuwa yanzu an tabbatar da mutuwar mutane 7, koda yake kuma an ceto wasu 7. Dukkan mutanen dake cikin jirgin, baya ga mutane biyu, sauran ‘yan kasar Koriya ta Kudu ne masu yawon shakatawa.

Gidan talabijin na kasar Hungary ya bada rahoton cewa dukkan mutane da aka ceto, an sallame su daga asibiti banda guda daya wanda ake jinyar sa saboda karyewar kashin hakarkari. 'Yan sandan kasar Hungary suna tsare da matukin jirgin ruwan mai suna Yuriy C.

  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jarida da ke aiki da Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA). Yana da kwarewa a fannoni da dama, da suka hada da shafukan yanar gizo, talabijin, bincike, rubutu da hotuna. Dan asalin kauyen Hiliya ne daga karamar Hukumar Tambuwar a jihar Sakkwato.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG