Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Alkalumma Na Nuni Cewar Jahar Kano Tafi Yawan Marasa Aikinyi


Alkalumma Na Nuni Cewar Jahar Kano Tafi Yawan Marasa Aikinyi

Anyi itifakin cewar rashin aikinyi yafi Kamari a jahar Kano a cewar hukumar samar da guraben aikin yi. Shi kuma shugaban shirye shirye na hukumar kyautata da’a ta jahar Kano Dr. Kabiru Musa Shu’aibu yace gwamnatin jahar Kano ta samar da guraben ayyuka ga matasa.

Yace duk matasa da suka halaci makarantun kimiya da fasaha, yanzu akwai damar daukansu aiki a ma’aikatar lafia, don yanzu haka gwamnati ta kirkiro da wani shiri da a ke kira Lafia Jari, kuma shi wannan shirin don a taimaka ma marasa aikin yi ne da kuma taimakama al’umma.

Kana kuma ta bangaren Mahauta gwamnati tasa anzabo mutane dubu goma wanda akabasu horo, wanda bayannan an basu jari wanda zai taimakamusu don su gyara sama’arsu da tsafta. Abu mai matukar mahimmanci shine gwamnati ta hana yawon bara, don haka kuma za’a samamusu sana’a da tayi daidai da su.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:00 0:00
Shiga Kai Tsaye

  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jarida da ke aiki da Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA). Yana da kwarewa a fannoni da dama, da suka hada da shafukan yanar gizo, talabijin, bincike, rubutu da hotuna. Dan asalin kauyen Hiliya ne daga karamar Hukumar Tambuwar a jihar Sakkwato.

XS
SM
MD
LG