Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

AMSOSHIN TAMBAYOYINKU Wutar Dajin Turai: *Shin Ta Na Da Alaka Da Zafi? *Me Ya Sa Ba Ta Cika Aukuwa A Afurka Da Aka Fi Zafi Ba?


Ibrahim K Garba
Ibrahim K Garba

Masu sauraronmu assalama alaikum; barkanmu da sake saduwa a wannan shirin na Amsoshin Tambayoyinku.

Tambaya:

Assalama alaikum Muryar Amurka. So na ke a yi min karin haske a kan wutar daji da ke aukuwa a wasu yankunan kasashen Turai:-

*Shin ko wannan wutar ta na da alaka da yanayin zafi da ake ciki?

*In har akwai alaka, to me ya sa wannan wutar ba a cika ganinta ba a kasashenmu na Afurka duk da yake cewa yanayin zafinmu ya fi na Turai?

Mai tambaya: Ado Turaki Askira, jihar Bornon Najeriya.

Amsar:

Idan Malam Ado Turaki Askira da ma sauran masu saurare na tare da mu, ga kashi na daya na amsar tambayarka game da gobarar dajin da aka fai yi a Turai. Wakilinmu a Adamawa, Muhammadu Salisu Garba, ya samo ma ka amsar ne daga Furfesan fannin yanayi, Abubakar Sadik Umar, na Jami’ar Modibbo Adama da ke Yola, jihar Adamawan Najeriya.

To sai a kasance da mu makon gobe don jin kashi na biyu kuma na karshe na wannan tambayar da kuma wasu tambayoyin. Yanzu a madadin Farfesan yanayi a Jami’ar Modibbo Adama, Abubakar Sadik Umar, da wakilinmu a Adamawa, Mohamed Salisu Garba, ni Ibrahim Ka-Almasih Garba ke cewa sai makon goben idan Allah ya kai mu. Wassalam.

Ga cikakken sautin shirin:

07-30-22 AMSOSHIN TAMBAYOYINKU.mp3
please wait

No media source currently available

0:00 0:12:27 0:00

XS
SM
MD
LG