Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Amurka Ta Taimakawa Kasashen G5 Sahel Da Kayan Aikin Soji


Kayan aikin soji da gwamnatin Amurka ta ba Jamhuriyar Nijar gudummuwa
Kayan aikin soji da gwamnatin Amurka ta ba Jamhuriyar Nijar gudummuwa

Gwamnatin kasar Amurka ta tallafawa rundunar hadin guiwar kasashen G5 Sahel da wasu kayayakin ayyukan soja a ci gaba da karfafawa dakarun wannan yanki guiwa a yakin da suke kwafsawa da kungiyoyin ta’addancin iyakokin kasashen Mali Burkina da jamhuriyar Nijer.

Motoci masu silke kimanin 22 kirar MAMBA hade da land cruiser 2 na amfanin aisibitin sojoji, da wasu kayayakin gyaran motoci masu sulke ne aka hannuntawa hukumomin tsaron wannan kasa a yayin wani bukin musamman da aka gudanar a birnin yamai.

Kayan aikin soji da gwamnatin Amurka ta ba Jamhuriyar Nijar gudummuwa
Kayan aikin soji da gwamnatin Amurka ta ba Jamhuriyar Nijar gudummuwa

Kayayyakin wadanda darajarsu ta haura miliyan 8 na dolar Amurka gudunmuwa ce daga gwamnatin Amurka domin amfanin bataliyar sojojin Nijer mai aiiki a karkashin rundunar G5 Sahel. Da yake jawabi a yayinda yake damka makulan wadanan motoci jakadan Amurka Eric P Whitaker ya bayyana burin ganin an shawo kan ayyukan ta’addanci a yankin.

Ya ce “Muna fatan kayayakin da muka bada zasu karfafawa Nijer guiwa a yukurinta na jibge kwararun askarawa masu aikin sintirin da zai karawa daukacin dakarun tsaro azamar aiki ta yadda za a tabbatar da tsaro akan iyakokin kasashen Mali Burkina Faso da Nijer.”

Da yake karbar wannan tallafi ministan tsaron kasar Nijer Pr Issouhou Katambe ya yaba da gudunmuwar da kasar Amurka ke baiwa wannan kasa da makwaftanta akai akai a fannonin da suka shafi sha’anin tsaro.

Kayan aikin soji da gwamnatin Amurka ta ba Jamhuriyar Nijar gudummuwa
Kayan aikin soji da gwamnatin Amurka ta ba Jamhuriyar Nijar gudummuwa

A watan fabrairun 2019 kasar Amurka ta baiwa jamhuriyar Nijer motoci masu silke kimanin 60 da treloli 4 da tankoki 2 na dakon mai 2 na ruwa ba’idin wasu runhunan tamfol da naurorin kariyar sojoji da na harakokin sadarwa a fagen daga a ci gaba da karfafa matakan yaki da kungiyoyin ta’addancin yankin sahel.

Saurari cikakken rahoton da wakilin muryar Amurka a Yamai Souley Moumouni Barma ya aiko mana cikin sauti.

Amurka Ta Taimakawa Jamhuriyar Nijar Da Kayan Aikin Soji-2:30"
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:11 0:00


  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG