Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Amurka Ta Yi Ikrarin Kashe 'Yan Ta'adda 15 a Somalia


Wani yanki da aka yi bore e Somalia a bara
Wani yanki da aka yi bore e Somalia a bara
Wasu hare-haren sama da dakarun Amurka suka kai a Somalia, sun halaka mayakan Al Shabab 15 da ke yaki da dakarun Afirka da na Somalia.
Kakakin rundunar dakarun Amurka ta AFRICOM da ke Afrika, Manjo Karl Wiest ne ya fadawa Muryar Amurka a karshen makon nan.
A cewar shi, mayakan na zama "babbar barazana" ga dakarun kasa da kasa, wandanda jami'an tsaron Amurka suka ce sun yi nasarar kwato garin Janaale da ke yankin Lower Shabelle.
Rundunar ta AFRICOM har ila yau ta fada a wata sanarwa da fitar cewa, ta kai wasu hare-hare guda biyar a tsakanin Litinin da Talata a kusa da yankin Janaale tare da hadin gwiwar gwamnatin Somalia.

Facebook Forum

Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG