Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Amurka Tace Ta Gaji Da Halin Kasar Rasha


Amurka tace ta “gaji da halin” Rasha, don haka ta tsinke yarjejeniyar da suka kulla game da kasar Syria, inda Amurkar ta bada hujjojin da suka hada da hare-haren da ake kaiwa kan yankunan dake shak da mutane fararen hula a kasar dake yankin Gabas ta Tsakiya.

Da yake bayyana cewa wannan “ba kuduri ne da aka dauka a saukake ba,” kakakin ma'aikatar harkokin wajen Amurka, John Kirby yace ba abinda Amurka bata yi ban a ganin cewa wannan yarjejeniyar tayi anfani, amma, a cewashi, “Rasha ta ki ta cika nata aiki” da ya shafi yarjejeniyar.

Kakakin yace Rasha ta kasa, ko kuma taki, ta matsawa gwamnatin Syria lambar tayi aiki da sharuddan dake kunshe a yarjejeniyar wadanda Rashar ta aminta da su, a maimakon haka, Rasha ta zabi yin anfani da karfin soja kawai.

To amma Rasha ta musanta wannan ikrarin na Amurka, inda jakadanta a MDD Vitaly Churkin yake cewa “in ba don Rasha ba, da yanzu ko ina ba abinda ake gani illa tutucin kungiyar mayakan ISIS ko ina a cikin Damascus, babban birnin kasar ta Syria.”

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG