Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Ceto Wadansu Jarirai A Jihar Imo Da Ake Sayarwa A Wani Gida


Wadansu mata masu ciki sun je awo a asibiti
Wadansu mata masu ciki sun je awo a asibiti

Rundunar 'yan sandan jihar Imo ta ceto kimanin jarirai da 'yan mata talatin da ake keta hakinsu a jihar Imo

Rundunar ‘yan sanda a jihar Imo dake kudu maso gabashin Najeriya ta ceto wadansu jarirai da kuma ‘yammata da dama a wani gida inda ake tsare mata bayan an yaudare su, sun shiga gidan, a kuma rika yi masu fyade domin su dauki ciki a sayar da jariran da suka haifa.

A cikin hirarsu da manema labarai, kwamishinan ‘yan sanda na jihar Mohammed Musa Katsina ya bayyana cewa, an shafe shekaru ana keta hakin bil’adama a wannan gidan, wanda aka sawa suna “Green House” ana kuma gudanar da sana’oi a kofar gidan kamar sauran gidajen dake kewaye ba tare da sanin abinda ke gudana a cikin gidan ba.

Bisa ga cewarshi, an sami kananan yara da dama a gidan wadanda dukansu shekarunsu basu wuce sha shida zuwa sha tara ba. Yace an sami jarirai da ‘yammata guda talatin a wannan gidan.

Ga rahoton da wakilinmu a yankin Naija Delta, Lamido Abubakar ya hada mana a kan wannan batun.
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:49 0:00
Shiga Kai Tsaye
  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG