WASHINGTON D C —
Masu zanga zangar kin jinin gwamnati a babban birnin Iraqi sun toshe manyan hanyoyi a birnin.
An kuma rufe makarantu da ofisoshin gwamnati a Baghadaza da kuma wasu biranen kasar a yau Lahadi, ranar aiki ta farko a mako a kasar da galibin ta musulmai ne, yayinda masu zanga zangar suka hau kan tituna suna neman sauye sauye a tsarin siyasar kasar.
A jiya Asabar masu zanga zangar sun yi gangami inda suka bijirewa matakin da gwamnati ke dauka akan su.
Dubban ‘yan Iraqi sun taru a filin Tahrir dake Baghadaza shekaran jiya Juma’a inda suka gudanar da zanga zangar kin jinin gwamnati mafi girma tun bayan da aka fara zanga zangar a watan da ya gabata.
Za ku iya son wannan ma
-
Afrilu 01, 2023
Ranar Talata Trump Zai Mika Kansa Ga Hukuma
-
Maris 29, 2023
Ukraine Ta Kaiwa Rasha Wani Mummunan Hari
-
Maris 29, 2023
Kasar Azerbaijan Ta kaddamar Da Binciken Harin 'Yan Ta'adda
Facebook Forum