Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Dauki Matakan Tsaro A Jihar Nassarawa Bayan Asarar Rayuka


Harin da makiyaya ke kaiwa a kauyukan Taraba
Harin da makiyaya ke kaiwa a kauyukan Taraba

Gwamnatin jihar Nasarawa tace ta dauki tsauraran matakan tsaro a yankin karamar hukumar Akwanga, bayan wani rikici da yayi sanadin rasa rayukan mutane goma sha shida a karshen makon jiya.

Lamarin ya auku ne a wani kauye mai suna Wuman, dake kusa da Andaha a karamar hukumar Akwanga, yayinda al’ummar Mada ke wani biki.

A cewar wani ganau da ya bukaci in sakaya sunansa, mutane goma sha shida ne ‘yan bindigar suka harbe har lahira.

Shugaban Kungiyar Miyetti Allah na jahar Nasarawa, Alhaji Muhammad Hussaini ya yi kira ga hukumomi su gudanar da bincike don gano wadanda suka aikata kisan, a kuma hukunta su.

Komishinan yada labaran jahar Nasarawa, Muhammad Jamil Zakari ya bayyana cewa, tuni gwamnati ta tura jami’an tsaro a yankin.

Saurari cikakken rahoton Zainab Babaji

Mutane 16 sun rasa rayukansu a Nassarawa-3:24"
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:24 0:00

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG