Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Fara Kada Kuri'a Kan Batun Karin Wa'adin Mulkin Shugaban Masar


Wani hoton kamfe
Wani hoton kamfe

Tun bayan da 'yan majalisun kasar Masar su ka amince da karin wa'adin shugaban kasar na ci gaba da zama a ofshinsa har zuwa 2030, yanzu haka al'ummar kasar da ke ciki da wajen kasar suma za su kada kuri'unsu kan lamarin.

“Ku yi abinda ya kamata, ku kada kuri'ar amincewa," wasu daga sakonnin da alamomin da aka kafa jikin gidaje a fadin birnin al-Khahira ke dauke da su kenan. Babu wani bayyanannen adawa.

Irin tallata manufarsu da masu goyon bayan gwamanti su ka yi din na kiran da a yi kwaskwarima ga kundin tsarin mulki don bai wa shugaban kasar Masar, Abdel Fattah el-Sissi, damar ci gaba da zama a ofishinsa har zuwa shekarar 2030.

Mutanan kasar Masar da su ke zaune a kasashen waje za su fara kada kuri’arsu a yau juma’a, kuma za a fara jefa kuri’a na kasa baki daya a gobe Asabar – kasa da sati daya bayan da ‘yan majalisa su ka amince da matakin.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG