Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Fara Kidayar Kuri'u Bayan Kammala Babban Zaben Ghana


Babban zaben Ghana
Babban zaben Ghana

Ranar Litinin 7 ga watan Disamba ne aka gudanar da zaben shugaban kasar Ghana da na ‘yan majalisar dokokin kasar mai kujeru 175.

Nan take bayan kammala kada kuri’a a babban zaben kasar ta Ghana da ke yammacin Afrika aka fara kidayar kuri’u, kuma ana sa ran nan bada jimawa ba za a fara samun sakamakon zaben.

Gabanin soma zaben wakilin Muryar Amurka Ridwan Abbas ya zagaya wasu cibiyoyin zabe inda masu kada kuri’a suka kafa dogayen layuka, wasu ma a nan suka kwana don su sami damar yin zabe saboda a cewarsu zaben na da muhimmanci.

Jami’an zabe a wasu cibiyoyi sun ce komai ya tafi daidai kamar yadda aka tsara, ko da ya ke an samu rahoton harbe-harbe a gundumar Awutu Senya da ke jihar tsakiya ta Ghana har wasu su ka jikkata.

Saurari cikakken rahoton Ridwan Abbas.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:29 0:00


XS
SM
MD
LG