Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Fara Samun Baraka A Jam'iyar APC, Jihar Kaduna


Tambarin jam'iyar APC
Tambarin jam'iyar APC

An sami baraka a jam'iyar APC a jihar Kaduna biyo bayan zaben Dr. Hakeem Baba Ahmed a matsayin sabon shugaban jam'iyar

Rahotanni daga jihar Kaduna na nuni da cewa, an fara samun baraka a sabuwar jam’iyar APC biyo bayan nada Dr Hakeem Baba Ahmed da wadansu mutane biyu a matsayin shugaba da sakatare da kuma ma’ajin jam’iyar na jiha.

A cikin hirarsu da wakilin Muryar Amurka Isa Lawal Ikara Mr. Mataimaki Tom Maiyashi daya daga cikin ‘ya’yan jam’iyar, ya bayyana bukatar sake salo.

Bisa ga cewar Maiyashi, idan ba an nemi hanyar dinke barakar aka kuma rungumi dukan ‘ya’yan jam’iyar ba, tana yiwuwa a sake komawa gidan jiya.

Shima Mallam Shu’aibu Lili daya daga cikin ‘ya’yan sabuwar jam’iyar CPC da ta narke ta koma APC. Yace an sha su sun warke saboda haka ba zasu yarda a sake maimaita kaura kuran da aka yi a lokutan baya a ya hana jam’iyar kai labari ba.
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:16 0:00
Shiga Kai Tsaye
  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG