Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Fara Shagulgulan Cikar Nijar Shekaru 58 Da Samun ‘Yanci


Ministan Cikin Gidan Nijar Bazoum Mohammed
Ministan Cikin Gidan Nijar Bazoum Mohammed

Hukumomi a Jamhuriyar Nijar sun kaddamar da bukuwan murnar cikar kasar shekaru 58 da samun ‘yancin kai.

A irin wannan lokacin bukuwa akan shirya wasannin motsa jiki da nuna al’adun kasar.

Za a kwashe kudan tsawon mako guda ana wadannan shagulgula, wanda a wannan karo birnin Agadez ne zai dauki nauyin yi.

Masu lura da al’amura sun ce daukan ragamar wannan biki da Agadez zai yi, ya taimaka ma wajen samun sabbin gin-gine.

Dama Agadez birni ne na masu yawon bude ido, inda mutane daga kasashen duniya ke ziyartar shi.

Bukuwan sun fara gudana ne a cikin kwararan matakan tsaro, inda gobe ake sa ran za a gudanar da pareti.

Saurari rahoton Yusuf Abdoulaye domin jin karin bayani:

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:59 0:00

XS
SM
MD
LG