Masarautar Doma da ke jihar Nasarawa ta bukaci al’umma ta taimaka wajen bai wa dakarun Najeriya bayanai da zasu kai ga kakkabe bata gari da samar da zaman lafiya a Najeriya.
A ranar Litinin ne Shelkwatar dakarun Najeriya ta kaddamar da tubalin gina wata shelkwata ta musamman a karamar hukumar Doma, jihar Nasarawa, wadda za ta samar da tsaro, musamman a yankin Arewa ta tsakiyar Najeriya da ke fama da ayyukan bata gari.
Mai Martaba, Andoma na Doma a jihar, Alhaji Ahamadu Aliyu Kauga, ya bukaci jama’a su bai wa dakarun sahihan bayanai da za su taimaka a kokarin da ake na ganin an samar da dawamammen zaman lafiya.
Shugaban kungiyar matasan Fulani ta Miyetti Allah a Jihar Nasarawa, Alhaji Bello Dauga Inusa, ya ce kasancewar rundunar zai kawo karshen tashin hankalin da suke fuskanta.
Shugaban kungiyar matasan Tivi a Jihar Nasarawa, Peter Ahemba ya ce zasu ba dakarun goyon baya a wannan kokarin da ake yi na samar da zaman lafiya.
Saurari cikakken rahoton cikin sauti daga Zainab Babaji:
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 27, 2021
An Saki 'Yan Makarantar Kagara Da Malamansu
-
Fabrairu 27, 2021
Lokacin Lallashin Masu Daukar Makami Ya Wuce- Buhari
-
Fabrairu 27, 2021
Tattaunawar Gumi Da 'Yan Ta'adda Ba Alheri Ba Ne - Dattawan Arewa
-
Fabrairu 27, 2021
Adadin Dalibai Mata 317 Aka Sace A Zamfara - 'Yan Sanda
-
Fabrairu 27, 2021
Jihohin Zamfara, Kano Sun Rufe Makarantun Kwana
Facebook Forum