Jiya Asabar Ofishin Jakadancin Amurka da ke kasar Saudiyya, ya gargadi Amurkawa da su yi kaffa-kaffa da wuraren da ke kusa da Fadar Al Salaam, bayan rahotanni sun nuna cewa an kai wani hari wurin.
Ministan Cikin Gida na Saudiyya ya fadi jiya Asabar cewa an kashe wasu dogarawan tsaron fadar biyu 'yan asalin Saudiyya baya ga wasu uku da su ka ji raunuka, bayan da wani mutum ya tuko wata mota zuwa mashigar sashin yamma ta Fadar Gidan Sarautar Saudi a Jeddah, ya shiga bude wuta.
Wani mai magana da yawun Ma'aikatar ya ce dogarawan tsaron fadar sun bindige maharin har lahira.
Mai magana da yawun Ma'aikatar ya ce maharin dan asalin kasar ta Saudiyya ne, mai suna Mansour al-Amri, dan shekaru 28 da haihuwa.
Facebook Forum