Mazauna Banjul, da kuma jami’an difilomasiya a babban birnin na Gambiya, sun bayar da rahotan barin wuta mai yawa a unguwar da fadar shugaban kasar take cikin wannan birni.
Wasu shaidun sunce suna kyautata tsammanin akwai hannun dakaru masu tsaron shugaba Yahya Jammeh a harbe harben da ya ‘barke a safiyar yau Talata a birnin Banjul.
Har yanzu dai babu wani tabbacin cewar wannan yunkurin juyin mulki ne, kuma an samu rahotannin dake sabawa juna a kan ko an kawo karshen wannan fadan.
Wani rahoto na cewa shugaban kasar Yahya Jammeh baya kasar alokacin da harbe-harben ke faruwa, ana tsammanin yana kasar Faransa ko Dubai.
Kasar Gambiya dai karamar kasace data samu ‘yancin kanta daga mulkin mallakan Ingila, tana makwabtaka da kasar Sanigal.
Shugaban kasar ya karbi mulki ne a shekara ta alif dari tara da casa’in da hudu a juyin mulki, wanda yake fuskantar suka kan batutuwa na keta hakkin bil adama.