Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Kashe Jami’an Tsaro A Jumhuriyar Niger.


Sojoji Najeriya kusa da Maiduguri, Mayu 14, 2015.
Sojoji Najeriya kusa da Maiduguri, Mayu 14, 2015.

An kashe wasu jami'an tsaro su biyu da rana tsaka a jamhuriyar Niger, sai dai an kasa gane ko wanene suka aikata wannan danyen aikin, amma jami'ai sunce suna nan suna gudanar da bincike

Wasu da ba’a san ko su wanene ba sun afkawa jami’an tsaro da rana tsaka a arewancin Jumhuriyar Niger kuma suka kashe su.

Rahottani sun ce anga wadannan mutane cikin mota kirar Pick-up, sai’lin da suka afkawa jami’an da aikin su farautan masu dauke da miyagun kwayoyi ko fasa kwabrin makamai, ko kuma sace mutane suyi garkuwa dasu.

Maharan dai ance su hudu ne kuma sun kashe jami’an tsaro biyu daga cikin sauran da ba bayyana adadin su ba.

please wait

No media source currently available

0:00 0:01:56 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG