WASHINGTON D.C. —
Hukumomi a Najeriya na bikin tunawa da ranar Majalisar Dinkin Duniya ta hanyar sake bude ofishin majalisar a hukumance a Abuja, babban birnin kasar.
Tun a shekarar 2011 aka rufe ofishin, bayan wani mummunan hari da mayakan Boko Haram suka kai ginin.
An bude ofishin ne a jiya Alhamis, shekaru takwas bayan da wani dan kunar bakin wake ya kutsa da mota cikin ginin, ya ta da bam.
A cewar karamin Sakatare na Majalisar Dinkin Duniya mai kula da fannin ayyukan jin-kai, Mark Lowcock, sake bude ofishin, wata alama ce da ke nuna cewa ba za a mika-wuya ga masu ayyukan ta’addanci ba, yana mai cewa, za su ci gaba da taimakawa Najeiriya wajen cin ma burinta na ganin ta samu makoma mai kyau da cikakken tsaro.
Za ku iya son wannan ma
-
Janairu 29, 2023
CBN Ya Kara Kwana 10 Kan Wa’adin Daina Karbar Tsofaffin Kudi
-
Janairu 27, 2023
Jirgin Kasan Kaduna Zuwa Abuja Ya Kauce Hanya
-
Janairu 27, 2023
Za Mu Daukaka Kara – Adeleke