Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Sake Samun Barkewar Rikici a Jihar Adamawa


ADAMAWA: Gwamnan jihar Adamawa Muhammad Jibrilla Bindo
ADAMAWA: Gwamnan jihar Adamawa Muhammad Jibrilla Bindo

Tun makon jiya aka shiga wani rikici tsakanin 'yan kabilar Bachama dake yankin Numan da makiyaya inda har aka samu asarar rayuka sai kuma gashi wani rikicin ya sake barkewa a yankin dake cikin jihar Adamawa

Wani jami'in 'yan sandan jihar Adamawa ya yiwa wakilin Muryar Amurka dake Yola, Ibrahim Abdulaziz, bayanin abubuwan dake faruwa.

Dangane da matakan da suka dauka a matsayinsu na jami'an tsaro ya ce sun baza mutanensu a duka kauyukan da aka kai hari da kewayensu. Ya tabbatar da samun labarin barkewar rikici a kauyen Dung dake cikin karamar hukumar Demsa. Ya ce hankulan sojojin sama da na kasa da 'yan sanda sun koma yankin. Injishi sun dauki duk matakan tsaron da suka kamata su dauka. Ya kara da kiran jama'a da su daina yin aiki da jita jita saboda wai sun samu wasu rahotanni amma da suka duba lamarin sai ya kasance sabanin abun da aka gaya masu.

A kan ko rayuka nawa suka salwanta jami'in tsaron ya ce bashi da labari. Sai dai ya yi alkawarin bada duk wani karin bayani da suka samu nan gaba.

Dangane da labarin cewa an tare hanyar zuwa Gombe daga Yola ana tsayar da motoci ana kashe mutane, jami'in ya karyata batun. Ya ce babu gaskiya ciki saboda motocinsu suna sintiri akan hanyar. Bugu da kari, sun kara jami'an tsaro a hanyar. Suna kuma jaddadawa jami'ansu su tabbatar ba'a samu irin wannan lamarin ba a hanyar.

Akan Savana tare da cewa an kona kamfanin Savana, har wa yau jami'in ya ce duk jita jita ne saboda akwai jami'ansu da yawa a yankin Savanan.

Ga rahoton Ibrahim Abdulaziz da karin bayani

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:32 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG