A wani cibaya, an kashe wasu mutane biyu a garin Barikin Ladi na jahar Filato, wadda a ‘yan shekarun nan ta shiga sahun jahohin da ke fama da tashe-tashen hankula. Kashe mutanen biyu ya biyo bayan dan kwanciyar hankalin da aka samu, bayan mummunar fitinar da ta tashi kwannan baya, wadda ta yi sanadin asarar rayuka da dama.
An kashe mutane biyun, wadanda masu sana’ar sayar da kayan miya ne, ranar Lahadi. Hasali ma, tuni kungiyar ‘yan kayan miya ta jahar Filato ta ce kashe wadannan mambobin na ta biyu da aka yi, wani koma baya ne ga jahar ta Filato, wadda har ta fara murmurewa kafin nan.
To sai dai duk da wannan abin takaici na kashe wadannan mutane biyu, har yanzu wasu shugabannin jama’a na kiran da akai zuciya nesa. Mataimakin shugaban kungiyar masu sayar da kayan gini a jahar ta Filato, Garba Ibrahim, ya yi kiran da a yi hakuri a yafe ma juna.
Ga dai Zainab Babaji da cikakken rahoton:
Facebook Forum