Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Yanke Hukuncin Gidan Kasu Ga Wasu 'Yan-Wasan Kasar Benin


Wata kotu a Jamhuriyar Benin ta yanke hukunci wa ‘yan wasan kwallon kafar kasar su 10, dake cikin tawagar 'yan kasa da shekaru 17, zuwa gidan maza saboda samun su da laifin yin karya dangane da ainihin shekarunsu na haihuwa.

Kotun wadda take zamanta a birnin Kotono, ta yankewa 'yan wasan hukuncin daurin wata guda ne wa kowannensu.

A watan Satumba ne dai aka kame 'yan wasan wanda suke ikirarin cewa, shekarun su na haihuwa kasa da 17 ne, bayan an gano cewar karya ce kawai suka sharara, wanda hakan yasa aka kore su daga cikin wasan neman tikitin halartar shiga gasar cin kofin Nahiyar Afrika na 'yan kasa da shekaru 17 da haihuwa sakamakon an musu gwajin kashi (MRI).

A shekarar 2004, hukumar ce idan ba'a mantaba ta FIFA ta taba haramtawa Jamhuriyar Benin shiga wasanni, saboda matsalolin cin hanci da rashawa da suka yiwa hukumar kwallon kafar kasar katutu.

Haka zalika tsakanin shekarar 2010 zuwa 2013, hukumar kula da wasan kwallon kafa ta FIFA, ta sha yiwa kasar gargadi da barazanar sake daukar matakin haramta mata shiga dukkanin wasanni, muddin ta gaza wajen gyara matsalolin da ke yiwa harkar kwallon kafa karan tsaye.

Wannan hukumcin ya hada da jami'an gudanarwa na manyanan 'yan wasan.

  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jarida da ke aiki da Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA). Yana da kwarewa a fannoni da dama, da suka hada da shafukan yanar gizo, talabijin, bincike, rubutu da hotuna. Dan asalin kauyen Hiliya ne daga karamar Hukumar Tambuwar a jihar Sakkwato.

Facebook Forum

Kofin Duniya ta Qatar 2022

Kofin Duniya ta Qatar 2022
please wait

No media source currently available

0:00 0:00:32 0:00
Karin bayani akan Kofin Duniya ta Qatar 2022

Ronaldo vs. Messi

Ronaldo vs. Messi
please wait
Embed

No media source currently available

0:00 0:01:24 0:00
Satumba 30, 2020

Ronaldo vs. Messi

Karin bayani akan Wasanni
XS
SM
MD
LG