Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ana ci Gaba da Fuskantar Karancin Mai a Najeriya


Wata ma'aikaciyar wani gidan mai a birnin Lagos, bayan da aka cire tallafin mai.
Wata ma'aikaciyar wani gidan mai a birnin Lagos, bayan da aka cire tallafin mai.

Rahotanni daga Badun fadar jihar Oyo ya nuna a can ma ana fuskantar karancin mai kamar a wasu manyan biranen kasar.

Wakilin Muriyar Amurka dake yankin Hassan Umaru Tambuwal, wanda ya gewaya wasu sassan birnin badun, ya iske mutane suna cikin layi fiye da sa’o’I biyar kuma basu sami mai ba.

Da yawa daga cikin wadanda ya zanta dasu sun bayyana cewa laifin daga mahukuntan kasar ne saboda basa adalci wajen tafiyar da al’amuran da suka shafi kyautatawa jama’a.

Wasu daga cikin wadanda ya zanta dasu, sun koka kan yadda masu gidajen mai suke kara farashin mai zuwa Naira 120 kan ko wani lita. A wasu wuraren sayar da ma farashin yana fin haka.

Idan za’a iya tunawa cikin makon jiya lokacinda aka fara fuskantar wannan matsala, jami’ai daga kamfanin hada hadar man fetur ta Najeriya NNPC, sunyi alkawarin cewa zuwa karshen makon jiya za’a daina fuskanatar wannan matsala.

A cikin ‘yan kwanakin nan ne ma ministar harkokin mai ta Najeriya Allison Madueke, ta ziyaci wasu gidajen mai inda ta yi zargin cewa dillalan mai ne suke haddasa karancin mai.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:47 0:00
Shiga Kai Tsaye
XS
SM
MD
LG